Showing posts with label ZAUREN KANNYWOOD. Show all posts
Showing posts with label ZAUREN KANNYWOOD. Show all posts

Sunday, November 24, 2019

RIKICI A KANNYWOOD LAIFIN NI DA ALI NUHU NE ADAM A ZANGO

RIKICI A KANNYWOOD LAIFIN NI DA ALI NUHU NE ADAM A ZANGO

Shahararren jarumi a masana'antar Fim ta Kannywood Adamu Abdullahi Zango wato (Adam A Zango) ya ce yaran sa da yaran Ali Nuhu sune ke haifar da matsala da rashin jituwa a Kannywood din.

Jarumi Adamu Zango ya bayyana haka ne a wata hira da aka yi da shi a Radio France International wato RFI.


Cikin wata tattaunawa da jarumin yayi da gidan Radio France International (RFI) ya bayyana cewa rikici da matsalolin da yaran sa dana fitaccen jarumi Ali Nuhu ke haifarwa a Kannywood ba laifin kowa ba ne sai shi da jarumi Ali Nuhu.

A cewar Adamu Zango da ace suna tsawatarwa ga yaran nasu to da zasu iya dakatar da su daga yin duk wani abu da zai haifar da rikici a masana’antar.

Jarumi Adam Zango ya kara da cewa ta bangarensa bai yadda yaransa su ci zarafin wani jarumi ba.

Idan zaku iya tunawa dai a watannin baya ne wani rikici ya kunno kai tsakanin manyan jaruman guda biyu wanda har sai da ta kai ga anje kotu, inda daga bisani kuma aka samu yin sulhu a tsakanin su.

Saturday, November 23, 2019

DAFA SHAYI NE GADO NA BA WAKA BA ADO GWANJA

DAFA SHAYI NE GADO NA BA WAKA BA ADO GWANJA

Jarumi a masana'antar Fim ta Kannywood kuma shahararren mawakin Hausa Ado Isa Gwanja ya ce ko kusa shi ba dan daudu ba ne.

Silar fitowa ta a matsayin dan daudu a Fim shi ne akwai wani Fim da aka bukaci dan daudu ciki aka nemi 'yan daudu jar su 50 cikin su aka rasa wanda zai iya shi ne sai aka ce bara to a gwada dan masana'antar ana gwadani kuwa na yi dace da wurin,

Wannan shi ne farkon fara fitowa ta a dan daudu inji Ado Gwanja,

Farko dai Ado Gwanja ya fara ne da rera wakoki kasancewar bai samu karbuwa ba sai ya juya akalar sa zuwa fito wa a Fim

Wakokin Gwanja dai sun fi karbuwa ne wajen mata kamar yadda zaka ji a mafiya yawan wakokin sa mata yafi ambata ymawakin ya ce yana yin haka ne sabo da su mata sun fi son biki ma'abota nishadi ne
To wa zan ambata idan ba mata ba?" A cewar sa.

Gwanja ya musanta zargin da ake yi masa cewa yana furta kalmomin batsa cikin wakokin sa a inda yace To ni dai da Hausa nake waka kuma bahaushe yana da fahimta a iya sani na a duk wakoki na ba abun da ya shafi batsa ko kusa,


Matashin ya fara waka ne kusan shekaru 10 da suka gabata
Ra'ayi ne ya sa na fara waka" a cewar sa.

Ya kara da cewa shi ba gadon waka yayi ba shige yayi sai Allah ya bashi baiwa har ya samu karbuwar da yake kai a halin yanzu,

Yace idan gado ne da dafa shayi zan gada domin shi ne sana'ar mahaifi na a Kano"



Kamar yadda yake a bayyane cewa mafi yawan jarumai ko mawaka na cin karo da matsaloli, sai dai Gwanja ya ce duk wanda ya samu kansa a matsala "to shi ya ga dama ya shige ta."
Kazalika mawakin ya ce shi a saninsa ba shi da wasu makiya ko abokan adawa a wannan harka, idan ma kuma akwai su to bai san da su ba. "Kazantar da ba ka gani ba kuma tsafta ce," in ji shi.


Thursday, November 21, 2019

RUKAYYA DAWAYYA A YANZU BANI DA SAURAYI A KANNYWOOD

RUKAYYA DAWAYYA A YANZU BANI DA SAURAYI A KANNYWOOD

A YANZU BANI DA SAURAYI a Kannywood cewar rukayya dawayya
Cikin shirin daga bakin mai ita da #BBC HAUSA suka kaddamar a yau sun yi hira ne da shahararriyar jaruma a masana'antar Kannywood wacce taga jiya taga yau wato Rukayya Umar wacce aka fi sani da Rukayya Dawayya.

Ga kadan daga cikin tambayoyin da aka yi mata da kuma amsoshin da ta bayar,


1 Wanene saurayin ki a Kannywood?

Rukayya. "A yanzu bani da saurayi a Kannywood"

2 Da wa koka taba yin soyayya a Kannywood?

Rukayya. "Misbahu Ahmad"

3 Wanene saurayinki na farko?

Rukayya. Kasancewar ba a Nigeria na girma ba na girma ne a kasar Saudiyya saurayi na na farko wani balarabe ne sunan sa Faisal".

4 Yaushe zaki sake aure?

Rukayya. Nan ba da dade wa ba"

5 Me kike fara yi idan kika tashi daga barci?

Rukayya. Kasancewar gidana hana da fadi nakan fito na zagaya ina duba filawowi sai na zauna na yi ta Azkar"

6 Yaruka nawa kika iya magana da su?

Rukayya. Yaruka 3 Hausa Larabci Fulatanci English.

Zamu dakata a nan sai wani lokaci na gaba.

Kuci gaba da bibiyar zaurenhausa a ko da yaushe.

Friday, November 1, 2019

Yadda Jarumi Ali Nuhu Ya Samu Karramawa A Kasar Indiya

Yadda Jarumi Ali Nuhu Ya Samu Karramawa A Kasar Indiya

A makon da ya gabata ne dai Jarumin masana'antar Fim ta Kannywood wato Ali Nuhu ya samu karramawa a kasar Indiya.

Ya samu karramawar ne daga wadansu dalibai 'yan Arewacin Nigeria da kuma malaman su Indiyawa a kasar ta Indiya bayan sun gayyace shi wani taron Al'adu

Daliban na karanta fannoni daban-daban kama daga fannin likita zuwa hada magunguna da injiniya da sauransu,” in ji Ali Nuhu kamar yadda ya shaida wa BBC. Jarumin ya ce baya ga wadannan dalibai, wasu makarantu a kasar sun ba shi lambobin yabo.

KARANTA WANNAN. Juruman 'Yan Mata 6 Mafiya Shahara A Kannywood

Ali Nuhu ya ce “Akwai makarantar Dayananda Sagar School of Physiotherapy su ma sun ba ni lambar yabo kuma sun nuna jin dadinsu kan yadda daliban Najeriya ke mayar da hankali kan karatunsu.”

Jarumin ya ce ya yi matukar farin ciki da wannan karramawa da kuma yadda malaman wadannan makarantu ke da sha’awar al’adun Hausawa. “Wadansu daga cikin malaman har fina-finan Hausa suke kallo saboda su ga yadda yanayin rayuwar Bahaushe take.

“Shi ya sa idan wani dan wasa ya zo taro irin wannan sukan karrama shi,” inji Ali Nuhu.


Wednesday, October 23, 2019

Rashin mijin aure ne ya kawo mun tsaiko Maryam Yahaya

Rashin mijin aure ne ya kawo mun tsaiko Maryam Yahaya

Shahararriyar jarumar Kannywood, Marayam Yahaya ta bayyana dalilin da yasa bata yi aure ba har yanzu.


A cewar jarumar rashin mijin aure ne ya kawo mata wannan tsaikon

A kwanakin baya ne Abubakar Bashir Maishadda ya bayyana cewa, Allah ne bai yi auren sa da jarumar ba"

Jarumar ta bayyana hakan ne a hirar da tayi da gidan rediyon Freedom dake Kano. Jarumar tace: "Da aure da mutuwa duk lokaci ne, idan lokaci kuwa yayi ai zan daga. Baabu mijin ne, hakan ne ya hanani auren. Ku fito ku aureni, kunsan aure maza yanzu wuya suke.

A kwankin baya ne dai hotuna suka dinga yawo a kafafen sada zumunta ana cewa, an kasa Maryam Yahaya don kuwa saurayinta Maishadda zai angwance da matashiyar jaruma Hassana Muhammad. Sai dai, a wata hirar da gidan rediyon Freedom yayi da Abubakar Bashir Maishadda, ya tabbatarwa da gidan rediyon cewa tabbas ya taba soyayya da Maryam. Amma Allah ne bai nufa zai aureta ba domin yanzu haka an kusa bikinsa. Shararriyar jarumar na daga cikin manyan jarumai da tauraruwarsu ke haskawa a masana'antar ta Kannywood.

Tuesday, October 1, 2019

Saturday, September 21, 2019

Sunday, September 15, 2019

Dalilin da yasa na daina fito wa a Fim Rashida Adamu

Dalilin da yasa na daina fito wa a Fim Rashida Adamu

Rashida Adamu tana daya daga cikin Jarumai mata a Kannywood musamman a shekarun baya kafin daga bisani ta shiga harkokin siyasa a inda ta kai ga har Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya bata mukami a gwamnatin sa,
A yanzu dai tana a matsayin mai bawa gwamnan na #Kano shawara kan harkokin mata hakan haifar da dakatar da ita daga sana'ar da aka santa da ita wato Hausa Fim,

Wace ce Rashida Adamu?

Anhaifi Rashida Admu a karamar hukamar Tarauni a jihar Kano ta yi karatun firamare a Taraunin a daga bisani ta wuce zuwa jihar Jigawa ta yi Sakandren mata a Garki daga nan ta wuce zuwa wata makaranta mai suna Ma'haj a kasar Sudan a inda ta yi karatun Diploma daga nan ta wuce wata makarantar Jami'a a birnin Kwatano dake kasar Benin ta yi digiri a bangaren kimiyyar siyasa daga baya ta dawo ta stunduma a harkar Fina-finan Hausa,

Fim din ta na farko shi ne Jariya sai kuma Fim din da ya fito da ita wato Sa'a wanda ita ce ta shirya shi da kudin ta
Taci gaba da firo wa a Finafinai kamar su Tutar so Gobe da nisa Halwa.,

A yanzu dai likafar Rashida ta ci gaba tun tana fito wa cikin fim din wadansu har ta kai tana yin nata na kanta a karkashin kamfanin ta har kuma yanzu ta zo ta shiga cikin harkar siyasa kuma Allah ya sanya mata  albarka aka bata mukamin Mai ba Gwamna Shawara kan Harkokin Mata kuma kasancewar wannan aiki ne na zuwa Ofis hakan ya sanya ta dakatar da fito wa a Fim sabo da karancin lokaci.



Saturday, July 27, 2019

Yan mata Sun fake da Fim ne suna neman maza Tanimu Akawu

Yan mata Sun fake da Fim ne suna neman maza Tanimu Akawu

Daya daga cikin dattijai na masana'antar Fim ta Kannywood ya yi hira da manema labarai a inda ya fallasa 'yan matan dake wannan harka,

Cikin tattaunawar da aka yi da shi Alhaji Tanimu Akawu a wani gidan radio ya yi bayanin cewa kimanin shekaru 'dai 'dai har goma sha takwas kenan yana sana'ar Fim a Kannywood amma bai mallaki dokiyar da wadansu 'yan mata suka mallaka cikin shekaru kadan ba.

Cikin hirar da akayi da Dattijon a wani gidan radio mai suna Human Right dake Abuja cikin wani shirin su mai suna DANDALIN FINA FINAI
Alhaji Tanimu ya bayyana cewa 'yan matan na Kannywood kawai suna bin maza ne kama daga masu kudi zuwa 'yan siyasa,

Tanimu Akawu ya ci gaba da cewa Motar da wata 'yar wasa take hawa a yanzu zata iya siyen motoci guda 10 da yake da su"

Yaci gaba da cewa, 'Yan matan sun mayar da Fim madubi ne, duk macen da kaji tace za ta yi harkar fim, tana so a haskata ne karshe ta fake da bin maza domin ta samu kudi."

Jarumin ya bayar da misali da wata sabuwar jaruma, a inda ya ce, "Kallo kawai ta zo yi aka sanyata a cikin fim, amma yanzu wayoyin dake hannunta sun kai na kimanin dubu dari takwas, kasan kuwa ba a fim ta samu wannan kudin ba, saboda nawa ne duka ake biya a fim din?"

Ya cigaba da cewa, "Ko ni yanzu bazan auri 'yar Fim ba, saboda na san abinda ke tafiya a harkar, yarinya tun ba ta da wayo take kallon mu muna yin fim amma yanzu ta zo cikin shekara daya ta samu kudin da bamu taba tunanin zamu samu ba, yaya za ayi ta dinga ganin girman mu."

Saturday, July 6, 2019

Mata 6 mafiya shahara a Kannywood

Mata 6 mafiya shahara a Kannywood

Kyawawan jaruman Kannywood guda shida,


Kamfanin fim na Kannywood ya sami albarka tare da kwararrun mata masu ban sha'awa da kuma basirar da suka dace da su.

Wadannan 'yan mata ba kawai suna da kyau ba amma suna aiki tukuru ,

RAHAMA SADAU
Rahama Sadau matashiyar jaruma ce mai hankali an haife ta a jihar Kaduna a ranar 7 ga Dismember Shekarar 1993, tana da digiri a harkar kasuwanci ta kasance daya daga cikin shahararrun 'yan wasan Kannywood bayan fim din ta da ake kira Gani Ga Wane Rahama Sadau tana da burin zama shahararriyar yar wasa kuma ta cimma burin ta,

HADIZA GABON
Hadiza Aliyu wacce aka fi sani da Hadiza Gabon tana daga cikin manyan yan wasan Kannywood kuma kyakkyawa ce matuka an haifeta a ranar 1 ga watan yuni a 1989 a garin Libreville a kasar Gabon ta fito cikin fim din Ali Yaga Ali,

NAFISAT ABDULLAHI
Nafisa Abdullahi yarinya ce kyakkyawa cikin yan mata na Kannywood kuma kwararriyar yar wasa an haifeta a garin Jos na jihar Filato ranar 23 ga watan Janairu shekarar 1990 Allah ya arzuta nafisa da fata mai kyau ta taka rawar gani cikin fim din Sai Wata Rana,

FATIMA ABDULLAHI
Jarumar da aka fi sani da Fati Washa ita ma kyakkyawa ce mai ban sha'awa kwarai da gaske an haifeta ranar 21 ga watan Faibrairun 1993,

UMMI IBRAHIM
Ummi Ibrahim da aka fi sanin ta da Zeezee jaruma ce kuma mai kudi da ta taka rawar gani a masana'antar ta Kannywood ta kasance cikin yan mata mafiya shahara a masana'antar masoyiya ce ga mawakin nan na kudu wato Timaya,

HAFSAT IDRIS
Hafsat da aka fi sani da Hafsat Barauniya ita ma tana daga cikin shahararrun mata a masana'antar Kannywood an haifeta a garin Shagamu ta fito cikin Fina-Finai daban daban ciki har da shahararren Fim din ta na Barauniya.

Sunday, June 30, 2019

Mutuwar Kumurci jita jita ce kawai

Mutuwar Kumurci jita jita ce kawai

Kamar dai yadda kowa ya sani ba wannan ne karo na farko da ake yada jita jitar mutuwa ga yan fim ba.

Kai bama yan fim ba ma ana yada irin wannan jita jita ta mutuwa ga duk wani mutum da yayi suna a kasa ko duniya baki daya

Misali zaka samu anyi irin wannan ga Malaman Addini ko yan siyasa ko mawaka kai har da yan kwallon faka.

Irin wannan jita jitar ce dai tayi ta yaduwa cewar wai jarumin fina-finan Hausa na kannywood shu'ibu lawal da aka sani da kumurci ya rasu to sai dai a wannan karon ma karya ce zunzurutu da wani ya zauna ya tsara da wata manufa da shi ne ya san ta

Alhaji Shu'ibu Lawal dai yana nan cikin koshin lafiya kamar yadda ya fito ya bayyana da bakin sa.


A wani video da ya bayyana tare da dan aura da suka dora a shafin Instagram jarumi Shu'ibu Lawal ya ce masu fatan mutuwa ta kuyi hakuri lokacin yana nan zuwa ko ku riga mu ko mu riga ku" kamar yadda yace: